Trump ya ce akwai 'babban taron' manema labarai a Pennsylvania

endsars

Shugaban Amurka Donald Trump, ya sanar da cewa akwai wani babban taron manema labarai anjima a Philadelphia, wanda shi ne birni mafi girma a Jihar Pennsylvania.

A wani saƙo da ya wallafa a baya, wanda tuni aka goge shi, ya bayyana cewa lauyoyi ne za su yi taron.

Ya bayyana cewa za a yi taron ne da misalin 11:30 agogon ƙasar, ƙarfe 16:30 kenan agogon GMT.

A yanzu dai ana jiran sakamakon zaɓe daga Pennsylvania, wadda ita ce jihar da Joe Biden ke buƙata a halin yanzu ya lashe zaɓen ƙasar.

A halin yanzu, Jam'iyyar Democrat wadda Mista Biden ɗin ke takarar a ƙarƙashinta na gaba a Jihar ta Pennsylvania da ƙuri'u 28.833.


Tags

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.